Ilimi Hasken Rayuwa

Yadda cire tallafin mai a ya shafi harkar ilimi a Najeriya

Informações:

Sinopsis

Shirin 'Ilimi Hasken Rayuwa' ya yi nazarari ne kan cire tallafin mai da sabuwar gwamnatin Najeriya karkashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu ta yi, inda a lokacin da ya ke gabatar da jawabi jim kadan bayan rantsar da shi, Tinubu ya sanar da janye biyan kudin tallafin mai da gwamnatin kasar ke yi, lamarin da ya sa farashin makamashin ya yi tashin gwauron zabi, kuma ya haifar da karin matsin rayuwa a kasar musamman a  bangaren marasa karfi. Iyaye da daliban abin ya shafe su, ganin yadda matakin ya tilasta wasu iyaye fara tunanin sauyawa 'ya'yansu makaranta sabida kasa iya ci gaba da biyan kudin motar da ake kai su makaranta don neman ilimi, a dayan bangaren ma, al'amarin ya shafi su kansu malaman makartu tun daga matakin Firamari da Sakandari da ma manyan makarantu.Ku latsa alamar sauti donjin cikakken shirin..........